An Ƙara Samun Adadin Mutum 108 Da Suka Mutu A Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Jigawa


An sake samun adadin mutane 108 da suka rasa rayukansu a sanadiyyar ambaliyar ruwan sama tun daga watan Agusta zuwa karshen watan Satumba.


RFI Hausa ta rawaito cewa, a ranar Asabar ne kakakin rundunar 'yan sandan jihar ta Jigawa Lawan Adamu ya tabbatar da adadin waɗanda suka rasa rayukansu a sanadiyyar rugujewar gine-gine, tsawa da kuma waɗanda ruwa ya cinye su.


Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnan jihar, Muhammad Badaru ya dawo daga balaguron da ya yi zuwa kasashen waje a ranar Juma’a, bayan da ya shafe makwanni 3.


Gwamna ya sha caccaka a kan yadda ya zabi ya yi balaguro a lokacin da mutanen jiharsa ke tsakar wannan bala’in, da kuma yadda ya gaza ziyartar yankunan da ambaliyar ta shafa.


Damunar bana an samu ambaliyar ruwa sosai a sassan jihohin arewacin Najeriya wanda hakan yai sanadin mutuwar mutane da dama da kuma lalata amfanin gona na tarin kuɗi masu yawa.

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post