'Ƴan Fashin Daji sun sace mata 60 a Jihar Zamfara

 


Garuruwa da dama ne wanda 'yan fashin suka kone a yayin harin da suka kai a cewar wani dan majalisa mai wakiltar yankin. 


KARANTA: Wani Mutum Daya Bata Sama Da Shekaru 60 Ya Bayyana A Garin Kano

KARANTA: Dalilai biyar da suka tabbatar da mutuwar Abubakar Shekau

KARANTA: Yadda Mutum 13 Suka Rasa Rayukan Su A Hadarin Jirgin Ruwa A Sokoto


Rahotanni daga jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya na nuna cewa 'yan fashin daji sun sace wasu mata kimanin su 60 a cikin wani farmaki da suka kai kan wasu kauyuka a ranar Talata. Kamar yadda shafin gidan Radio Bbc Hausa suka rawaito. 


A cewar wani ɗan majalisar wakilai dake daga yankin, ya bayyana cewa an sace matan ne daga kauyen Manawa yayin da aka kashe mutane hudu a kauyukan Malele da Randa a Karamar Hukumar Maru.


Hon. Shehu Ahmed S. Fulani dan majalisa mai wakiltar yankin da abin ya faru a majalisar wakillan Najeriya ya shaida wa sashen gidan radio na BBC Hausa cewa garuruwa da dama ne ƴan bindigar suka ƙone a yayin kaiharin.


Ya Kara da cewa maharan sun tafi da matan ne bayan mazajensu sun gudu a lokacin da suka kawo harin.
Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post