Kalaman Da Ya Dace Duk Magidanci Yayi Amfani Dasu Bayan Ya Gama Saduwa Da Iyalinsa




Ba duk maza suke iya furtawa matansu kalamai na kambamawa ko na godiya ba bayan da suka kammala kwanciyar aure dasu.


Wasu Mazan ma ture matan nasu daga jikinsu suke yi bayan sun gama jin dadi dasu. Wanda hakan ba daidai bane.


Ga wasu kalamai guda 12 da suka dace duk wani magidanci ya furtawa matarsa su bayan kammala saduwan aure.


1: Na Gode: 

2: Allah Ya Miki Albarka:

3: Naji Dadinki Fiye Da Jiya:

4: Kin Kaini Wata Duniyar Ta Daban:

5: Ke Ta Dabance A Dadi:

6: Kin Jikani Da Ruwa Har Kirjina:

7: Allah Ya Barmu Tare:

8: Bazan Iya Jimirin Rasa ki Ba:

9: Allah Ya Yiwa Ungozomarki Albarka:

10:  Shi Yasa Bana Koshi Dake:

11: Kinada Tsafta:

12: Da Fatan Ban Ji Miki Ciwo Ba:


Wadannan kalmomin ba na godiya kadai bane. Suna kara kauna da soyayya a tsakanin ma'aurata.


Kada ka gama saduwa da matarka ba tare da ka furta mata wani kalmar da zai sa taji tayi dacen miji ba.


Akwai kalmomi da damar gaske da zaka iya amfani dasu maimakon kawai ka mike ka saka wandonka.


Wadannan kalmomin tamkar cewa kake ka gode da mutum da zai maka kyauta. Yadda mai kyauta ba zai jidadin rashin yi masa godiya ba. Haka ita ma mace bazata ji dadin idan mijinta ya kasa furta mata kalmar godiya bayan saduwa da ita ba.

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post