Malamin Jami'a Da Ya Rabawa Dalibansa 10 $100 Kowanen Su Ya Magantu


Tun a ranar Litinin ne dai wani labari ya karade shafukan sada zumunta kan cewa wani Malamin jami'a Bisi Olawuyi na jami'ar gwamnatin tarayya dake Ibadan ya rabawa dalibansa su 10 $100 Kowanen su. 


Sai dai a yammacin ranar Talata ne malamin ya fito a shafinsa na Twitter ya bayyana labarin da mara tushe da asali, domin shi baisan wannan magnar ba a sakon da ya wallafa Kamar haka. 


"Hankalina ya karkata ga wani sako na twitter da ke yawo cewa na baiwa dalibai 10 $100 kowanne. Wannan ba gaskiya bane ta kowace hanya. Da fatan za a yi watsi da wannan labari mara tushe. Na gode." 

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post