'Yan Bindiga Fiye Da Dubu 70 Suka Ajiye Makamansu A Arewa Maso Gabas


Christopher Musa wanda shine Shugaban Operation Hadin Kai a arewa maso gabashin Najeriya yace  akalla 'yan ta'adda dubu 80 ne suka mika wuya ga rundunar Sojin Najeriya. 


Musa ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a birnin Maiduguri a wata tattaunawa da yai da manema labarai kan nasarorin da rundunar ke samu a baya-bayan nan. 


Kwamandan ya ce ci gaba da kai hare-haren da ake kai wa 'yan tada kayar baya  su ka mika wuya.


A cewarsa, hakan ya sa a ka bukaci a samu karin sansanoni a Maiduguri domin karbar tubabbun da aka ware domin tantance maharan da wadanda ba mayakan ba.


Ya yaba da goyon bayan da jama’a ke ba su, wanda ya bayyana a matsayin “jarumai ” ya kuma bukace su da su ci gaba da dagewa wajen ganin an kawo karshen rikicin cikin gaggawa.


Muna matukar farin ciki da yadda jama’a ke ba mu hadin kai; suna ganin ikhlasi a cikin abin da muke yi.


Mun himmatu wajen bin ka’idojin kare hakkin dan Adam da ka’idojin tafiyar da ayyukanmu,” in ji  Musa.


A baya-bayan nan daina tawagar sojin Najeriya da hadin gwiwar operation hadin kai suna samun galaba a gumurzun da suke yi da 'yan bindiga. 


Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post