Dan Takarar Shugaban kasa A Jam'iyar APC Bola Tinubu Ya Gana Da 'Yan Kannywood


Dan takarar shugabancin kasa a karkashin inuwar jam'iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu tare da mukarraban yakin neman zabensa sun tarbi tawagar masu shirya fina-finai Na Najeriya.


Jaruman shirya fina-finan sun hadar da na Kudu da kuma na Arewa wato Nollywood da Kannywood.


Minista Hajiya Ramatu Tijjani Aliyu ita ce ta jagoranci jaruman masana'antar shirya fina-finan a wajen wannan ganawa da aka yi dasu.


Yayin ganawa dasu Bola Ahmed Tinubu ya nemi hadin kansu domin zamowarsa sabon shugaban kasar Najeriya a shekarar 2023.


Idan za a iya tunawa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya taba zama gwamnan jihar Lagos a shekarun baya.


Daga Suraj Na'iya Kududdufawa

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post