Wata Mata Ta Yanke Azzakarin Mijinta Ta Soye Shi



An kama wata mata mai suna Dayane Cristina Rodrigues Machado akan zargin ta na kashe mai gidan ta tare da yanke mazakutarsa ta soye. 


KARANTA: Mulkin Soja Ake Yi A Kaduna Ba Dimokuradiyya Ba, Isa Ashiru

KARANTA: Yan bindiga sun sace jarirai a Zaria

KARANTA: Duniya Na Fuskantar Tsadar Abinci Mafi Muni A Cikin Shekara 10


Jaridar Aminiya ta rawaito cewa matar mai shekara 33, an kama ta ne a garin Sao Goncalo na yankin kasar Brazil a ranar 7 ga Yunin bana bayan gano gawar mijinta mai suna Andre.


An kira ’yan sanda zuwa gidan ma’auratan a Unguwar Santa Catarina kuma sun iske gawar tsirara an yanke wasu bangarori na jikinsa.


’Yan sanda sun samu wuka a wurin da ake zargin ta aikata kisan ce, inda alamu suka nuna cewa, ita ce ta kashe mijin ta kuma ta yanke wasu sassan jikinsa.


An kama Machado a wurin kuma tun daga lokacin aka zarge ta da kisan kai. 


A cewar  wani gidan kafar labarai ta UOL, sun bayyana cewa ma’auratan sun fita zuwa gidan cin abinci a daren da aka aikata kisan, sai rikici ya barke a tsakaninsu.

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post