Yunkurin juyin Mulki A Najeriya 1990 Da Korar Jihohi 5 Daga Najeriya - Android Pols



A Rana mai Kamar Ta Yau a Lahadi  22 Ga Watan Afrilu 1990 An yi Yunkurin juyin mulkin a Najeriya, wani yunkuri ne na juyin mulkin da sojoji suka yi a Najeriya a ranar 22 ga Afrilun 1990 a lokacin da wani bangare na hafsoshin Sojin kasar, karkashin jagorancin Manjo Gideon Orkar, sukayi yunkurin hambarar da gwamnatin Janar Ibrahim Babangida.


Dakarun Sojoji masu Yunkurin juyin mulkin sun kwace gidan rediyon FRCN da ofisoshin sojoji daban-daban a kewayen Legas, ciki har da hedkwatar sojoji da gidan shugaban kasa a Barrack Dodan. Babangida yana wurin lokacin da aka kai hari a barikin amma ya samu nasarar tserewa ta baya, amma Harin Ya Ritsa da ADC din Babangida, Kanar UK Bello an kashe shi.


A cikin jawabin juyin mulkin da Orkar yayi ya kori wasu jihohi biyar na arewacin Najeriya Daga Kasar, ya zargi Babangida da shirin Nada kansa a matsayin shugaban Najeriya Na Mutu ka Raba, ya zargi gwamnatin mulkin soja ta tarayya da mayar da al’ummar Neja Delta saniyar ware da daukacin Kudancin kasar.


A cikin Takarda da ya karantawa al’ummar kasar ta hanyar watsa shirye-shirye kai tsaye da misalin karfe 4 na safiyar ranar 22 ga Afrilu, 1990, ya yi sanarwar korar jihohin Arewa mai nisa daga Najeriya, jihohin sun hada da Bauchi, Borno, Katsina, Kano da Sokoto. Masu fashin baki dai na ganin cewa Wani bangare na dalilin rashin nasarar juyin mulkin shi ne yadda kabilanci da kuma son zuciya da suka rika yadawa a jawabansu na juyin mulkin. hafsoshin sojojin Arewa sun yi gangamin goyon bayan Gwamnatin Tarayya a lokacin da suka gano cewa Wata makarkashiya ce da aka kulla don Wargaza Tarayyar Kasar.


Duk da yake, ana Tsammanin cewa Manjo Gideon Orkar ne ya shirya juyin mulkin, amma a lokacin Aiwatar da shari’ar juyin mulkin na ranar 22 ga Afrilu, 1990 wasu shaidun sun nuna cewa shi dan kanzagi ne kawai ba shi ne asalin wanda ya shirya juyin mulkin ba. Manyan Masu Ruwa da tsaki a shirin juyin mulkin sun hada da Laftanar Kanar Anthony Nyiam, Manjo Saliba Mukoro, Manjo Cyril Obahor a matakin karshe na shirin juyin mulkin ne suka dauki Orkar a cikin shirin. Haka kuma dole a ce hamshakin attajirin dan kasuwa Cif Great Ovedje Ogboru (Wanda Yayi Takarar Gwamna A Jam'iyar APC A Jihar Delta 2019) shi ne babban wanda ya taimaka da kudi don juyin mulkin.


An kama daruruwan mutane da suka hada da wasu fararen hula bayan yunkurin juyin mulkin, adadin wadanda suka mutu a rikicin da ya barke tsakanin dakarun masu Yunkurin juyin mulkin da dakarun gwamnati da kuma aiwatar da hukuncin kisa da aka yi bayan shari’a, ya sanya ta zama Yunkurin juyin Mulki juyin mulki mafi muni a tarihin Najeriya. Orkar da sojoji 41 daga cikin ’yan ta’addar nasa sun yi arangama da dakarun gwamnati bayan An Wargaza shirin Nasu an Kamasu kuma An same su da laifin cin amanar kasa. A ranar 27 ga Yuli 1990, an kashe su ta hanyar harbi.


Ga jerin Sunayen Wadanda Aka Kashe ta Hanyar Harbi 


1, Major Gideon Orkar

2, Lieutenant Awokoya E Akogun

3, Captain Nimibibowei Harley Empere

4, Lieutenant Cyril Okuser Ozoalor

5, 2nd Lieutenant Arthur Bandenyintite Umukoro

6, Staff Sergeant Julius Itua

7, Sergeant Martins Ademokhai

8, Sergeant Pius Ilegar

9, Lieutenant Nicholas Odey

10, Captain Perebo Aboela Dakolo

11, WO2 Monday Bayefa

12, Lance Corporal Jephthan Inesai

13, Corporal Sunday Effiong

14, Lance Corporal Francis Ogo

15, Lance Corporal Samuel Mbasue

16, Lance Corporal Albert Ojerongbe

17, Lance Corporal Geofrey Deesiiyira

18, Lance Corporal Emmanuel Aiyemola

19, Sergeant Stephen Iyeke

20, Corporal Joseph Efe

21, WO2 Afolabi Moses

22, Lance Corporal Idowu Azeez

23, Lance Corporal Vitalis Udzer

24, WO2 Jonathan Ekimi

25 Staff Sergeant Solomon Okunbawa

26, Private Richard Isaghohi

27, Staff Sergeant Barnabas Jarikpe

28, Private Egwola Makpamenkun

29, Lance Corporal Adegamen Friday

30, Private Monday Esebawen

31, Private Nnadi Mogaha

32, Sergeant Etim Umoh

33, Ex-Corporal Wasiu Lawal

34, Ex- Lance Corporal Ekominar Makililo

35, Ex- Lance Corporal Peter Umuyoma

36, Ex Sigralman Goodluck Emefe

37, Ex-Staff Sergeant Sampson Idejere

38, Sergeant Jolly Agbodowei

39, Lance Corporal Samuel Obasayi

40, Private Osazuwa Osifo

41, Lance Corporal Goodluck Ofojarere

42, 2nd Lieutenant Emmanuel O Alade

43, 2nd Lieutenant F J Esuku

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post