Yanzu-Yanzu: Rarara ya saki sabuwar waƙa kan zaɓen Gwamnan Kano - Android Pols



Zazzafar muhawara ta ɓarke a kafafen sada zumunta sakamakon sabuwar waƙa da fitaccen mawaƙin siyasar nan na APC Dauda Kahutu Rarara ya fitar kan zaɓen Gwamnan Kano.


A cikin waƙar dai Rarara ya jaddada furucin Gwamna mai barin gado Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya kira sakamakon zaɓen da Tangal-tangal.


Rarara ya kuma yi suka ga jam'iyyar NNPP da jagoranta lamarin da ya fusata mabiyanta musamman a kafafen sada zumunta.


Tun bayan sanar da sakamakon zabe wanda Hukumar INEC ta bayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben Kano ba'a sake jin duriyar mawaki Rarara ba sai yanzu. 

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post