Takaitaccen Tarihin Julius Sello Malema - Android Pols



Julius Sello Malema ɗan siyasa ne kuma ɗan gwagwarmayar Afirka ta Kudu wanda ɗan majalisa ne kuma shugaban jam'iyyar Economic Freedom Fighters, jam'iyyar hagu wadda ya kafa a 2013. A baya ya taba zama shugaban kungiyar matasa ta African National Congress Youth League daga 2008. zuwa 2012.


An haife shi a 31 Ga Watan Maris 1981Julius Malema ya kasance mamba a jam'iyyar ANC tun yana dan shekara tara  har zuwa lokacin da aka kore shi daga jam'iyyar a watan Afrilun 2012. Julius ya yi fice a matsayin mai goyon bayan shugaban ANC, sannan kuma shugaban Afirka ta Kudu, Jacob Zuma. Zuma da Firayim Ministan Lardin Limpopo, Cassel Mathale, sun bayyana shi a matsayin "shugaban nan gaba" na Afirka ta Kudu. 


An samu Malema da laifin kalaman kiyayya a watan Maris na 2010 da kuma a watan Satumba na 2011. A watan Nuwamba 2011, an dakatar da shi daga Jam'iyar ANC na tsawon shekaru biyar saboda haddasa rarrabuwar Kawuna a cikin jam'iyyar. A cikin 2011, an sake yanke masa hukuncin nuna kiyayya bayan ya rera waka " Dubul' ibhunu " ("Shoot the Boer "), hukuncin da aka amince da shi bayan daukaka kara, wanda ya kai ga fitar da shi daga jam'iyyar ANC. 


A shekara ta 2012, an tuhumi Malema da laifin zamba, halasta kudin Haram Bayan dage shari'ar sau da yawa, Kotun ta yi watsi da shari'ar a cikin 2015 saboda samun jinkiri da yawa da Hukumar Shari'a ta kasa ta yi, wanda ya haifar da tunanin cewa tuhumar na da nasaba da siyasa. Duk da haka, kungiyar kare hakkin Afrikaner AfriForum ta sanar a cikin 2018 cewa za ta gurfanar da Malema kan zargin cin hanci da rashawa.


Malema, Mopedi an haife shi kuma ya girma a Seshego kusa da Polokwane, Lardin Transvaal da ake kira Limpopo. Mahaifiyarsa tana aikatau a gidan musu hannu da shuni. Ya shiga Jam'iyyar African National Congress(ANC) 'Masupatsela yana da shekaru tara ko goma. Babban aikinsa a lokacin shi ne cire fosta na jam'iyyar National Party.


Ilimi


Malema ta kammala karatun sakandare a Mohlakaneng High School, Seshego , Limpopo. A 2010, ya kammala digiri na shekaru biyu a kan ci gaban matasa ta Jami'ar Afirka ta Kudu (UNISA). A shekara ta 2011, ya yi rajista a UNISA don samun digiri na farko na Arts a Sadarwa da Harsunan Afirka, kuma ya kammala a watan Maris 2016. A 2017, ya sami BA (Honours) a Falsafa daga UNISA. A halin yanzu yana karatun digiri na biyu a Jami'ar Witwatersrand.


Farkon sana'ar siyasa


An zabi Malema a matsayin shugaban kungiyar matasa reshen Seshego da kuma shugaban yankin a shekarar 1995, A 1997 ya zama shugaban kungiyar Congress of African Students (COSAS) na lardin Limpopo, kuma aka zabe shi a matsayin shugaban kungiyar na kasa a shekara ta 200. A cikin 2002, Malema ya jagoranci zanga-zanga COSAS ta daliban makaranta, ta Johannesburg; An gudanar da tattakin da tashe-tashen hankula da sace-sace.


Zaben shugaban kungiyar matasan ANC


An zabi Malema a matsayin shugaban kungiyar matasan ANC a watan Afrilun 2008, inda ya samu kuri'u 1,833 yayin da Saki Mofokeng ya samu kuri'u 1,696. Zaben - da taron - sun kasance da tsoratarwa, wanda daga baya Malema ya bayyana "halayen da ba su dace ba".


A lokacin zaben shugaban kasa na Afrilu 2009, Malema ya Nuna goyon bayan Zuma, inda Malema ya ce: "A shirye muke mu dauki makami mu kashe saboda Zuma". Bayanin nasa dai ya zama Abin yin Allah wadai daga 'yan siyasa da kuma 'yan Afirka ta Kudu baki daya, yayin da jam'iyyun adawa ke nuna alamar tambaya kan dalilin da ya sa Zuma bai tsawatar wa Malema ba. 


Daga baya aka sake zaben Malema ba tare da hamayya ba a karo na biyu a ranar 17 ga Yuni 2011 a Gallagher Estate a Midrand lokacin da Lebogang Mail, wanda shi kadai ne mai adawa da shi, ya ki amincewa da nadin. 


Satumba 2009 Rigimar Nedbank


A watan Satumban 2009, Malema ya yi barazanar zaburar da mutane don su janye asusunsu na Nedbank bayan bankin ya yanke shawarar janye tallafinsa daga gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta Afirka ta Kudu (ASA). Ko da yake Nedbank ya bayar da hujjar cewa an yanke shawarar ne bayan rashin gamsuwa da isar da abubuwan da suka faru a baya.


Oktoba 2012 Ziyarar Zimbabwe


Malema ya ziyarci Zimbabwe a watan Oktoban 2012 domin halartar wani daurin aure da kuma yin jawabi ga bangaren matasa na jam'iyyar ZANU-PF. Jaridar Mail and Guardian ta Johannesburg ta nakalto jaridar Herald Online ta Zimbabwe a wani labari, inda ta ce Malema ya shaidawa taron cewa: “Ya ce matasa a Afirka ta Kudu suna kira ga turawa da su mika wuya ga albarkatun kasa da ma’adanai da suke rike da su domin a lokacin da suka zo daga Turai ba su taho da komai ba. 


Kalamai na adawa da ANC


A wata hira da kafar yada labarai ta kasa da kasa Al Jazeera English da aka watsa a ranar 24 ga watan Afrilun 2016 Malema ya bayyana cewa idan jam'iyyar ANC mai mulki ta ci gaba da yin kakkausar suka ga zanga-zangar, "mu [EFF] za mu kawar da wannan gwamnati ta hanyar bindiga". Ya ci gaba da zargin jam'iyyar ANC da shan kaye a zaben 2014 a lardin Gauteng tare da tafka magudi har ta kai ga samun nasara. Bayan wadannan kalamai ne jam'iyyar ANC ta tuhume shi a shari'ar cin amanar kasa ga hukumar 'yan sandan Afirka ta Kudu kan Malema saboda yin kalaman. 


An san Malema da iya magana. Ya auri budurwarsa da suka dade tare a cikin wani biki na sirri a karkashin tsauraran tsaro a garinsu Seshego a shekarar 2014. Sun haifi dansu na farko Munzhedzi a 2016.  An haifi dansu na biyu Kopano a 2018. Har ila yau , Malema yana da ɗa mai suna Ratanang wanda suka haifa da Farkarsa Maropeng Ramohlale.

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post