Har yanzu dai nine Gwamna, ka bari a rantsar da kai mana - Martanin Ganduje ga Abba


Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya yi kira ga zaɓaɓɓen Gwamnan jihar Engr. Abba Kabir Yusuf da yayi haƙuri kar ya tsoma baki a al'amuran Gwamnati har sai an rantsar da shi.


A wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labaran Kano Malam Muhammad Garba ya fitar, ya yi martani kan shawarar da Abban ya bai wa masu gine-gine a filayen Gwamnati.


Ya ce, a kundin tsarin mulkin ƙasa har yanzu Dr. Ganduje ne Gwamna ba Abba ba, har zuwa ranar rantsuwa.


Saboda haka a yanzu duk abin da Gwamna yayi nasa ido ne, sai dai ya bari in an rantsar da shi sai yayi duk sauye-sauyen da zai yi.


Sanarwar ta ce, kuma fitar da filaye ai ba kanta farau ba, domin sanannen abu ne har a Gwamnatin da shi zaɓɓen Gwamna yayi aiki da ita a baya, wato dai Gwamnatin tsohon Gwamna Kwankwaso.


A ƙarshe sanarwar ta nemi waɗanda suka mallaki filayensu bisa ƙa'ida a ƙarƙashin Gwamnatin da su kwantar da hankalinsu.


Me zaku ce?

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post