Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bada Umarnin cigaba da amfani da tsohuwar Naira 200


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bai wa babban bankin ƙasar umurnin ya sake fito da tsofaffin takardun naira 200 domin a ci gaba da mu'amala da su a ƙasar.


Shugaban ya bayyana haka ne a cikin jawabin da ya yi wa al'ummar ƙasar da safiyar ranar Alhamis.


Buhari, wanda ya ce yana sane da irin halin wahala da al'ummar ƙasar ke ciki, ya ce za a ci gaba da amfani da takardar kuɗin ta naira 200 har zuwa 10 ga watan Afrilu.


Ya kuma buƙaci al'umma da su ƙara haƙuri kan halin da ake ciki.

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post