AL'AJABI: Wani dan Najeriya ya auri mata tagwaye a rana daya


Wani dan Najeriya ya auri wasu ’yan uwa mata tagwaye a unguwar Ede da ke jihar Osun. Hotuna da faifan bidiyo sun karade shafukan sada zumunta.


Dan jarida, Sikiru Obarayese, wanda ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter, ya ce an daura aurensu ne a ranar Asabar, 29 ga watan Oktoba.

 

Wata majiya ta gano cewa tagwayen sun auri mutumin ne saboda ‘ba za su iya rayuwa ba tare da juna ba’.


Kalli bidiyon yadda aka gudanar da daurin auren.


Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post