YANZU-YANZU: Ankashe Wani sojan Najeriya A kan hanyar Abuja zuwa lokoja, Sun tafi da matar sa


'Yan bindiga da ake zargin masu satar mutane ne sun kashe Manjo Janar Hassan Ahmed, wanda ke da babban matsayi na sojojin Nijeriya yayin da suke kan hanyar Abuja zuwa Lokoja.


Rundunar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Alhamis lokacin da ‘yan bindigar suka far wa motar babban jami’in. Sahara Reporters 


KARANTA: Shawarwari 52 Zuwa Ga Matan Aure, Zawarawa Da 'Yan Mata

KARANTA: Halin Kuncin Da Mutanen Kaduna Ke Fuskanta Ya Dame Ni El-Rufai


Wata majiya ta ce lamarin ya faru ne a daren ranar Alhamis a yankin Abaji, inda ta kara da cewa maharan sun kuma yi nasarar sace matar sa.


An gano cewa ma'auratan suna zuwa daga Okene lokacin da aka kai musu hari.


'Yan bindigar sun bude wa motarsa wuta ne sannan suka tafi da matar.


Kakakin rundunar, Brig Onyema Nwachukwu, ya ce, "Tare da cike da damuwa, babban hafsan sojojin, Laftanar Janar Faruk Yahaya, hafsoshi da sojoji na Sojojin Nijeriya sun yi nadamar sanar da rasuwar Manjo Janar Hassan Ahmed, tsohon shugaban Marshall na sojojin Najeriya.


"Abin bakin ciki ya faru ne lokacin da wasu 'yan bindiga suka far wa motar babban jami'in yayin da yake kan hanyar Lokoja zuwa Abuja a ranar 15 ga watan Yuli.


“Wata tawaga daga Hedikwatar rundunar karkashin jagorancin shugaban tsare-tsare  Maj Gen Anthony Omozoje sun ziyarci dangin matar da sauran‘ yan uwan mamacin.


“Membobin kungiyar matan hafsoshin sojojin Najeriya (NAOWA) karkashin jagorancin mataimakiyar shugaban kasa, Misis Stella Omozoje suma sun ziyarci iyalen don yi musu ta’aziyya.


"Za a yi jana'izar babban jami'in da ya mutu a makabartar Lungi Barracks ranar Juma'a."

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post