Yadda Ƴan bindiga suka kashe ƴan sanda huɗu a jihar Zamfara



A jihar Zamfara dake arewa maso yammacin Najeriya rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da mutuwar jami’anta guda hudu.




 

Sashen Hausa na BBC ya rawaito cewa lamarin ya faru ne a yayin wata arangama da ‘yan bindiga lokacin da suke aikin sintiri a yankin Rini cikin karamar hukumar Bakura.


Haka kuma ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyukan Tataka da Takalmawa a karamar hukumar Zurmi inda ake fargabar fiye da mutum 20 sun mutu tare da kwashe ɗumbin dukiya a karshen makon da ya wuce .


A yan kwanakinna dai Hare-haren 'yan bindiga sun dawo sosai a jihar Zamfara. 


Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post