Mayakan ISWAP Sun Mamaye Al'ummar Borno, Sun Afkawa Sojojin Najeriya


Mayakan ISWAP Sun Mamaye Al'ummar Borno, Sun Afkawa Sojojin Najeriya


KARANTA: Hadin Sa Kishiya Tagumi

KARANTA: An Cafke Wani Mutum A Sakamakon Yiwa 'Ya'yansa Mata Fyade

KARANTA: An Kashe 'Yan Bindiga 10 A Zamfara


Wasu ‘yan bindiga da ake zargi mayakan IS ne na yankin Afirka ta Yamma wanda akafi sani da (ISWAP) a halin yanzu suna cikin wani yanki na kudancin jihar Borno.

Mummunar kungiyar ta’addancin ta mamaye garin Damboa gari mai nisa da misalin karfe 10:30 na safe, tare da dimbin motocin su masu silken bindiga, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito. 

Lamarin ya jefa garin cikin rudani yayin da mazauna yankin da wadanda suka rasa muhallinsu ke gudun ceton rayukansu.


A cewar jaridar, an yi ruwan bama-bamai ta sama domin taimakawa sojojin kasa da na sa kai na cikin gida.


“Ina iya tabbatar muku cewa a halin yanzu wadannan yaran (ISWAP) suna kai hari ga sojojin jihar a garin Damboa. An kunna Airpower don tallafawa sojojin. Komai yana karkashin iko, ”inji majiyar tsaron.


Garin Damboa yana da nisan kilomita 100 daga Maiduguri, cibiyar matattarar 'yan tawaye.


Kwanan nan ISWAP ta karbe ikon kungiyar Boko Haram karkashin jagorancin Abubakar Shekau, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post