Ba zai yiwu a ga wata ranar Talata a Najeriya ba, azumi 30 za'ayi


Ba zai yiwu a ga wata ranar Talata a Najeriya ba, amma dai a duba: Kwamitin duban wata


KARANTA: Ainihin dalilin da ya sa Buhari ya dakatad da Hadiza Bala Usman

KARANTA:Mace mai haila zata iya yin kowace ibadah a watan Ramadan

KARANTA:Buhari, wasu mutanen basa ganin Alherin Gwamnatina, komai mukayi sai su kushe


Da alamun azumin 30 Musulmai zasu yi a bana, yayin da kwamitin duban wata tace ba zai yiwu a ga wata ranar Talata a Najeriya ba. 

Ranar Talata aka bada umurnin duba watan, duk da haka Kwamitin duban wata na majalisar koli ta shari'ar Musulunci a Najeriya ta sanar da cewa ganin jinjirin watan Shawwal ranar Talata, 29 ga watan Ramadana da kamar wuya.


A bayanin da kwamitin tayi ranar Asabar a shafinta na Facebook, ta bayyana cewa an yi hasashen ko wata ya bayyana zai fito ne gabanin faduwar rana, saboda haka ba zai yiwu a ga jinjirin wata ranar Talata a Najeriya ba.

Amma duk da haka jama'ar Musulmi a fadin Najeriya su fita neman jinjirin wata saboda yin hakan ibada ne.

Ranar Talata, 11 ga Mayu ya yi daidai da 29 ga watan Ramadana da ake fara neman jinjirin watan Shawwal na shekarar 1442AH.

Daga Jaridar Muryar 'yanci

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post