HALACCIN KALLON MATAR DA KAKE SON AURA

 


HALACCIN KALLON MATAR DA KAKE SON AURA


HADISI ya Tabbata Manzon Allah (ﷺ) Yana Cewa:


عن جابر بن عبد الله قال : قال رسول الله صلى الله عليه وسلم : ( إذا خطب أحدكم المرأة فإن استطاع أن ينظر إلى ما يدعوه إلى نكاحها فليفعل ) 

{أبو داود: ١٨٣٢}


 An Kar6o Daga Jabir Bn Abdallah (ra) Yace: Manzon Allah (ﷺ) Yace: {Idan Ɗayanku Yama Neman Mace da Auren Mace, Idan Ya Samu Daman Kallon Abinda Zai Sanya Masa Son Aurenta To Ya Kalla}.

(Abu-Daud: 1832)


Imam Shafi'i (RH) Yana Cewa: (Idan Mutum Zi Auri Mace Ne, To Ya Halatta Ka Kalli Fuskarta da Tafukan Hannunta Kaɗai)

(Al-Hawy Al-Khubra:9/ 34)


Ibn Ãbidin Yana Cewa: (Ya Halatta Ka Kalli Fuskar Matar da Kakeson Aura da Tafukan Hannunta Da Kuma Diddigen Ƙafarta. Baya Halatta Kallon Wurin da Waɗannan ba)

[Hashiyatu Ibn Abidin: 5/325).


Har Wa Yau Imam Ahmad (RH) Yana Cewa: {Ya Halatta A Kalli Abinda Galibi Yake Bayyana a Jikinta. Kamar Wuyanta da Hannunta da Makamantansu. Ibn Ƙudama (RH) Ya Hikaito Hakan a Cikin Littafinsa Al-Mugny: 7/454).


YA ALLAH MAZAN DAKE NEMAN MATA KA AZURTASU DA MATA NAGARI. HAKA KUMA MATAN DA BASU DA AURE KA BASU MAZA NAGARI.


✍🏽Abu-Aysha Al-Maliky

Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post