GASKIYAR ABINDA YA JAWO FADAN HAUSAWA DA YARABAWA A IBADAN


Wannan hoton yarinyar Da kuke gani sunanta Nana Aisha, tace a gaban I
Idonta aka fara Sanadin tashin
hankalin birnin Ibadan, inda ta tabbatar da cewa wani fan kasar niger ne ya zuba tumatur dinshi a bakin shagon wata bayarba ita kuma tace sai ya wanke mata shago shi kuma yana bata hakuri kafin ya samo ruwan wankewa, kawai wani bayarbe na zaune a gefe yakasa hankuri yasa bakinshi inda nan take bayarben ya mare dan niger din shi kuma ya rama inda bayarbe ya zube kasa sumamme yan uwanshi suka dauke shu zuwa asibiti inda lokitoci suka tabbatar musu da cewa bayarben ya mutu,

Amma abin mamaki sai kawai yarbawa suka kama daukar fansa ga 'yan uwansu' yan nigeria, abin suje sudau fansa ga 'yan kasar Niger tunda shine akayi fada fashi,


Anya daman yarbawa ba jiraye suke da Hausawanmu na Arewa dake zama can ba?

Muna kira ga shugabbannimu da sukaje gurin gwamnan oyo a jiya  karsu yarda sudawo har sai sun tsaya ankwatowa 'yan uwanmu hakkokinsu,

Kuma muna kira ga gwamnatin tarayya tasa a binciko wadanda suka yi wannan ta'addanci duk inda suke domin a hukuntardasu.


Suleiman Inuwa

I am a professional website developer and also an SEO expert.

Post a Comment

Previous Post Next Post